Tarihin Dr. Nasiru Yusuf Gawuna.

1 2,981

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

An haifi Dr Nasiru Yusuf Gawuna a ranar 6 ga watan Agusta, shekarar alif 1967 a karamar Hukumar Nassarawa ta Jihar Kano ga wani Malamin addinin Musulunci Malam Yusuf, kuma ya samu tarbiya da ke tattare da daukar nauyin koyo da girmama kowa.

Gawuna ya halarci makarantar firamare ta Gawuna, Kano a shekarar 1973 kuma ya samu shaidar kammala karatunsa na farko a shekarar 1979.

Daga nan ya wuce Makarantar Sakandaren Gwamnati da ke Gwaram a shekarar alif 1979 sannan ya wuce Makarantar Kimiyya ta Dawakin Kudu a shekarar alif 1981. Ya kammala karatunsa na sakandare a shekarar alif 1984.

A tsakanin shekarar alif 1984 zuwa 1985, ya shiga Makarantar Koyon Ilimi ta Jami’ar Ahmadu Bello, dake Zariya inda ya samu shaidar karatun share fagen jami’a, kafin daga bisani ya samu gurbin shiga Jami’ar Usman Danfodiyo da ke Sakkwato a shekarar alif ta 1985 kuma ya kammala karatunsa na BSc (Honours) a Biochemistry. A shekarar alif 1990.

Kwarewar aikin Gawuna ya fara ne a shekarar alif 1991 a lokacin da yake hidimar ƙasa wato (NYSC) a Cibiyar Kiwon Lafiya ta Gabashin Najeriya, Awkunanu a Jihar Enugu.

A shekarar alif 1992 zuwa 1994 Ya kasance Mataimakin Jami’in Zabe a Hukumar Zabe ta Kasa.

A shekarar alif 1995, Nasiru Yusuf Gawuna ya yi aikin asibiti a matsayin Masanin fasaha a Hukumar Kula da Asibiti na tsawon shekaru tara.

A shekara ta 2004, ya tsunduma cikin harkokin siyasa inda aka zabe shi shugaban karamar hukumar Nassarawa, dake Kano.

Siyasarsa ta fara ne da Shugaban Karamar Hukumar a Nassarawa dake Kano har karo na biyu inda ya jajirce wajen samar da jinya kyauta ga daukacin al’ummar Karamar Hukumar Nassarawa inda ya ajiye makudan kudade a dukkan manya da ƙananan asibitocin lafiya. Ya kuma yi nasarar bayar da tallafin karatu kyauta ga daukacin daliban karamar hukumar. Ya samar da ayyukan yi ga matasa.

Gawuna ya kuma hada kai da NDLEA domin daƙile masu shan miyagun kwayoyi a karamar hukumar, Ya samar da motocin bas ga kananan makarantu da manyan sakandare, ya gina ajujuwa da yawa da asibitocin gida.

A lokacin yana Shugaban karamar hukumar Nassarawa, shi ne na farko a jihar Kano da ake yi wa lakabi da “Maliya” Don haka ya zama wajibi a yi magana kan asalin ci gaban dan Adam da nufin karfafawa matasa gwiwa da zaburar da su kan abubuwan da suka shafi zamantakewa da ya samar.

Ya kasance kwamishina a lokacin mai takalmin karfe kuma kwamishina guda daya wanda ke kulla alaka da takwarorinsa ko da ba su cikin jam’iyya daya.

Nasiru Yusuf Gawuna
Hoto Daga Twitter

Yana mutunta duk tsohon ubanin gidansa kamar su Malam Ibrahim Shekarau Sardaunan Kano wanda ya rike mukamin shugaban karamar hukumar da kuma Dr Injiniya Rabi’uMusa Kwankwaso wanda a karkashinsa ya rike mukamin kwamishinan gona.

A karkashin Gwamna Ganduje ya rike mukamin Kwamishinan Noma, kuma a karshen wa’adin farko ne Gawuna ya zama sabon mataimakin gwamnan jihar Kano cikin al’ajabi bayan murabus ɗin Farfesa Hafizu Abubakar.

A jiya Litinin ne dai Gwamnan Kano Ganduje ya tabbatar masa da takarar gwamnan jihar Kano, inda a wurin yake daɗa nuna nagartar sa da kuma riƙon amanarsa.

Bidiyo daga Abubakar Aminu Ibrahim

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

  1. Hafnaz says

    Kamanta baka rubuta ƙabilar shi ba, pls Inason sanin ƙabilar shi

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »