online slot malaysia Takaitaccen tarihin Jaruma Ummi Rahab

Takaitaccen tarihin Jaruma Ummi Rahab

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Jaruma Ummi Rahab na ɗaya daga cikin ƴan mata masu ƙananan shekaru a masana’antar kannywood, ta fara harkan fim tun tana ƙasa da shekaru goma, jarumin kannywood (ADAM A ZANGO) ne ya shigar da ita cikin masana’antar fim. Inda aka fara haskata a fim ɗin jarumin mai suna “Kin Zamo Takwara Ummi “

An haifi Ummi Rahab a ranar 7 ga watan Afrilu na shekarar alif 2003 a Jihar Kaduna. Jarumar ta yi firamare da sakandire duk a jihar Kaduna. A yanzu haka tana zaune a jihar Kano don sana’ar wasan kwaikwayo.

Ummi Rahab

Fim din da ya haskaka jarumar shi ne fim ɗin “Kin Zamo Takwara Ummi”. Inda ta fito a ƴar gidan jarumi Adam A Zango.

Related Posts
1 of 15

Jarumar ta kasance ƙarama. Amma ta sami damar nuna cewa zata iya wasan kwaikwayo. Tun daga nan kyakkyawar jarumar ta zama sananna a masana’antar, a tsakanin tsofaffi da kuma matasa. Bayan wasu shekaru tabar masana’antar don cigaba da karatun ta na Sakandire.

Related Posts
1 of 14

Ummi ta dawo masana’antar tana da shekaru 18 a duniya. Jarumar ta dawo gabaɗaya don ci gaba da sana’arta ta fim. A wannan karon, Ummi ta ƙara girma kuma tauraron ta na haskawa a masana’antar.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

- Advertisement -

1 Comment
  1. […] post Takaitaccen tarihin Jaruma Ummi Rahab appeared first on Alummar […]

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »
online slot malaysia