Yadda Za’ayi Maganin Olsa (Ulcer) Komai Karfin ta.

9 18,734

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Olsa (Ulcer) cuta ce dakan addabi Al’ummar wannan zamani da muke ciki wanda zaka samu yawanci ana ɗauke da ita, wanda wasu mutanen sun san ita ke damunsu wasu kuma basu sani ba.

Akwai alamomin da olsa (Ulcer) take dashi dayawa wanda wasu da dama basu san cewa itake damunsu ba. Don haka Zamu kawo wasu daga cikin alamomin cutar Olsa (Ulcer) kamar haka:

  • Ciwon Ciki,
  • Amai mai tsami,
  • Jiki ya Dinga Rawa Idan Kanajin Yunwa,
  • Rashin Son Cin abinci,
  • Yawan yin Gyatsa,
  • Ciwon Ƙirji,
  • Kashin Jini,
  • Ramewa,
  • Kasalar Jiki,
  • Zafin Ƙirji.


Dadai sauransu domin akwai wasu da dama

Yadda Za’a Magance ta.
Ga masu Olsar dabata zama Chronic ba wanda sukeji zafin ƙirji ko ciwon ciki.

Zasu nemi Ayaba mai kyau babba guda ɗaya idan kuma ƙarama aka samu guda biyu sai ayi blending dinta ko kuma a kirɓa ta sosai.

Sai ku samu madarar ruwa kota gari kowacce iri saiku haɗa Ayaba da madara kamar cikin kofi guda sai a dinga sha da safe kafin aci abinci, bayan kayi kamar mintuna 30 dasha sai kuci abincin ku. Sai kuma kofi guda bayan anci abincin dare.

Ina Allah ya yarda wannan Ciwo zai warke da yardar Allah.

SAI KUMA MASU BABBAR OLSA (ULCER) WATO CHRONIC.

Zaku Nemi:

  • Habbatussauda,
  • Garin Magarya.
Habbatussauda
Habbatussauda

Zaku nemi Habbatussauda mai kyau a kasuwa, zaku dakata sosai tazama gari, saiku kawo garin Magarya a haɗa a dinga tafasa a saka zuma a ciki a dinga sha Safe, Rana da kuma dare.
Shima wannan Indai an maida kai to Insha Allahu za’a rabu da ita.

zaku iya Kallon Bidiyon bayanin kai tsaye fatan kuma zakuyi subscribe na youtube channel ɗinkin.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

  1. […] post Yadda Za’ayi Maganin Olsa (Ulcer) Komai Karfin ta. appeared first on Alummar […]

  2. Muhammed mustapha lawan says

    Masha allah naji dadin kasancewa da wanna shafi mai al.barka wajan taimakawa al.umar musilma

  3. Abubakar Bello says

    Aslm malam Allah bada lada Amma ayabar danyene,ko nunanne sannan za,ayi amfanidashi da bawunne ko a,a ataimaka ayimana bayani dalladalla

    1. alummarhausa says

      Wa’alaikumussalam Ayabar Nunanniya Ake bukata, sannan kuma a cire Bawon jikinta.

  4. Ibrahim Abbas says

    Allah yasaka da alkhairi, tambaya, garin magarya(ganyen ko yayan) ko duka za’a hadesu

    1. alummarhausa says

      Ya’yan Magarya din ake nufi

  5. Rabiu Umar Muhammad says

    Muna godiya Mal Allah Ya saka da Alkhairi.
    Ya’yan da ake sha za’a daka kokuma bayan an shanye sai a daka kwallon?

  6. Nazeef almansur says

    Allah ya saka da Alkhairi kuma yasa muga amfanin abin.

  7. BELLO says

    KWANA NAWA ZA AYI

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »