Takaitaccen Tarihin Jaruma Maryam Yahaya

0 3,391

Maryam na daya daga cikin fitatun jaruman shirya finafinan Hausa dake Kano wanda tauraron ta yake haskawa a wannan zamanin.

An haifi jaruma Maryam Yahaya a ranar 17 ga watan Julin shekarar alif 1997 a Goron Dutse dake Jihar Kano.

maryam yahaya

Jarumar ta taso da matukar son fitowa a shirin fina finan Hausa, wanda yawan kalon finafinan Hausan ya dada sanyata son kasancewa daya daga cikin yan wasan Hausa.

Jarumar ta fara wasan Hausa a shekarar 2016 inda ta fito a fim dinta na farko mai suna Gidan Abinci da kuma fim mai suna Barauniya, yayin da ta taka yar karmar rawa a finafinan.

Maryam tasamu shahara sosai a wani fim mai suna Mansoor wanda Jarumi Ali Nuhu ya bada Umarni.

Kyaututtuka

Maryam Yahaya tasamu kyaututuka da dama

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »