online slot malaysia Tarihin Jarumi Adam A Zango (Usher) Ko (Gwaska).

Tarihin Jarumi Adam A Zango (Usher) Ko (Gwaska).

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Adamu Abdullahi Zango wanda akafi sani da Adam A Zango, Usher ko Gwaska shahararran dan wasan Hausa ne a Kamfanin shirya fina-finan Hausa dake Kano, kuma mai shirya fina-finai, Mawaki, Dan Rawa.

HAIHUWARSA:


An haifi Jarumi Adam A Zango wanda akan yawan kirashi da (Usher) ko (Gwaska), a ranar 1 ga watan ogas din shekarar alib 1985, a karamar hakumar Zangon Kataf dake jihar Kaduna, tare da mahaifinsa Malam Abdullahi da kuma mahaifiyarsa Hajiya Yelwa Abdullahi.

Related Posts
1 of 14

KARATUNSA;


Adam A Zango yayi Firamari a shekarar alib 1989 sanan ya gama a shekarar alib 1995, sanan ya fara makarantar sakandire a shekarar alib 1996 sannan ya gama a shekarar 2001.

Tarihin Jarumi Adam A Zango (Usher) Ko (Gwaska).

RA’AYINSA GAME DA KARATU


Adam A Zango bai kammala wata Jami’a ko Polytechnic, domin a cewarsa samun wani kwalin Digiri ko makamancin haka bashine yafi muhimmanci ba matukar mutum zai iya samar da wata gudunmawa a kansa da Alummar da suke tare dashi, kuma ya koyi wani abu daga garesu sannan shima ya sanara dasu wani ilimi dayasani, wannan shine Ilimi.

A cewar Adam A Zango yanda matukar sani akan lamarin rayuwa, kuma ni mai ilimi akan abubuwa da nasani, bawai lallai sai mutum ya mallaki takaddar Digiri ko sama da Digiri ba.

Related Posts
1 of 13

KIDA DA WAKAR ADAM A ZANGO.


Lamarin Adama A Zango akan kida da waka kuwa ya faro asali ne tun lokacin da yana makarantar Sakandire, tun lokacin Adam A Zango yake wakiltar makarantasu.

Zango

SHIGA MASANA’ANTAR SHIRYA FINA-FINAN HAUSA.


Adam A Zango yashiga masana’atar shirya fina-finan Hausa a shekarar 2001, a mai kida, rawa da kuma rubuta waka. Sabo da amfaninsa a masana’antar sai ya fara fitowa a fim a matsayin karamin Jarumi, Adam A Zango yayi finan-finai sama da guda Dari (100).

ZAMAN GIDAN YARI.


A 2007 ne dai Adam A Zango aka yanke masa zama a gidan yari sakamakon karya doka da yayi na sakin wani Bidiyo mai suna Bahaushiya.

BAJINTAR DA YAYI WACCE BAZAA MANTA DA ITABA


A watan Oktobar 2019 ne dai Adam A Zango ya biya wasu makudan kudade da sukakai Miliyan Arba’in da Bakwai , ga Maryu don taimakawa karatunsu, kuma yaje har fadar maigirma Sarkin Zazzau Alh. Shehu Idris ya gabatar da kyautar.

Haka kuma a shekarar 2019 ne dai Adam A Zango ya bayyana kansa a wanda yafi kowa tasiri a kasar Hausa.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

- Advertisement -

1 Comment
  1. Murtala sani says

    Allah yakara daukaka adam azango aduniya da lahira

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »
online slot malaysia