Takaitaccen Tarihin Mudi Spikin

1 1,767

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

An haifi Alhaji Mudi Spikin a ranar 1 ga watan Oktoba 1930, a unguwar Darma da ke birnin Kano. Yayi karatun qur’ani a hannun Malam Umaru Badamagare. Bai taba zuwa makarantar boko ba, amma duk da haka, ya zauna jarrabawar GCE Ordinary level, ta hanyar yin rijista da wata kwaleji a Ingila, acikin 1960.

Ya sami illimin zamani ne a hannun abokansa na gwagwarmayar siyasa irinsu; Malam Sa’adu Zungur, Malam Aminu Kano, da kuma Alhaji Yusuf Maitama Sule.

Yana cikin mutanen da suka kafa jam’iyyar kwato yancin talaka wato NEPU a 1950. Ya fara rubuta wakokinsa tun a 1948, ya fara da wakarsa ta “Rasha Abokan Tafiya”, da kuma wani raddi da yayiwa malaminsa, wato malam Sa’adu Zungur maitaken “Arewa Jamhuriya Kawai”.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

  1. Audu says

    Yayi sosai

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »