TARIHIN ALIYU MAI BARNO

6 4,810

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

An haifi Mallam Aliyu Mai Bornu ne a shekarar 1919 sannan ya fara makaranta firamari a shekarar  ta 1932. Daga baya aka koma da shi makarantar sakandare ta Yola daga nan ya tafi kwalejin Kaduna a shekarar ta 1938 sannan  ya kamala karatun sa a shekara ta  1942 bayan ya cancanci ya zama Malami Mai koyar da Ingilishi.

Mallam Mai Bornu ya koyar da Ingilishi a makarantar, Yola Middle School daga shekara ta 1942 zuwa 1946 sannan ya koma  zuwa Kwalejin Kaduna inda  yaci gaba da koyarwa a shekara ta 1954, sannan kuma ya yi aiki a matsayin Mai Kula da Gidan  Makaranta a Veterinary School  kafin nan ya tafi  zuwa Jami’ar Bristol duk dai a shekara ta 1954, don nazarin tattalin arziki (Economics).

Bayan kammala karatunsa a shekarar 1957, ya dawo Najeriya ya kuma yi aiki tare da ma’aikatar kula da jama’a ta Arewacin Najeriya a matsayin Babban Jami’in Gudanarwa inda ya rike mukamai daban-daban kafin nan yasamu zuwa Babban Bankin Najeriya a 1959 a matsayin Mataimakin Sakatare a CBN.

Mallam Mai Bornu ya ci gaba da zama Mataimakin Sakatare  kafin nada shi Mataimakin Gwamna a shekarar  ta 1962. Ya zama Gwamnan Babban Bankin farko  a shekarar ta  1963 kuma ya yi ritaya daga aikinsa a shekarar 1967.

Daga baya aka nada shi Darakta gami da  Janar Manajan Kamfanin Taba  na Najeriya wato (NTC). Kodayake ya yi murabus da nadin nasa na NTC a shekarar 1969, ya ci gaba da kasancewa mamba a kwamitin gudanarwa har zuwa rasuwarsa.

Mal Aliyu Mai Barno ya rasu   a ranar 23 ga Fabrairu, 1970.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

  1. Muryar Hausa24 says

    Da kyau

  2. Arewa Boss says

    Allah ya saka da alkhairi

    1. Abdul says

      Amin Thuma A
      Min

  3. Habibu aliyu galadima says

    Allah yakara daukaka

  4. Nuruddeen says

    Allah kara daukaka

    1. alummarhausa says

      Ameen

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »