Takaitaccen Tarihin Marigayi Malam Aminu Kano

0 911

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Haihuwa

An haifi marigayi Malam Aminu Kano a shekarar 1920 a birnin Kano a Unguwar Dukawa, ya fito daga zuriyar Fulanin Gyanawa mahaifinsa Malamine kuma alkali, ya halarci makarantar Elementary ta Shahuci daga nan ya wuce kwalejin tarayya ta Katsina, Marigayi malam Aminu kano yayi karatun Al-qur’ani mai tsarki a wajen Shehun Malami, Malam Halilu, Malam Halilu shine limamin sarkin Kano Abdullahi Bayero a shekarar 1929 zuwa 1953.

Wani abokin Mallam Aminu kuma almajirinsa a siyasa, marigayi malam Lawan Dambazau a wani dan karamin littafi da ya rubuta a kan tarihin Mallam Aminu Kano, wanda ya sanya wa suna Dan Arewa na ai’nahi Mallam Aminu Kano.” A littafin Mallam Lawan Dambazau ya bayyana abubuwa biyar Mallam Aminu ya kuduri aniya ta fuskar zaman duniya, amma daga karshe babu wanda ya samu, sai a cikin wanda ba ayi zato ba. Ya rayu har ya rasu a ciki wato shugabanci da siyasa.

Da farko ya so ya zama Lauya, amma saboda sanin halinsa sai maganar ta girgiza (Resdan) na Kano na waccan lokacin, domin kowa ya san halin Mallam Aminu Kano na yaki da akidun turawa na danniyya da zalunci tun yana dan makaranta a “Middle.” Don haka in ya samu dama ya zama Lauya, to zai fituni turawa a kan bakin mulkin mallaka. Saboda haka sai aka dakile maganar ba taje ko’ina ba.

Na biyu; sai ya ce yana so ya zama likita nan ma aka ce babu isassun yaran da za’a hada su, su je Legas makaranatar koyan aikin Likita da ke Yaba Legas.

Na uku; sai ya ce yana so ya yi aikin dan-sanda, nan ma sai aka ce masa tsawon sa bai kai ba da inci shida (6).

Na Huɗu; sai ya ce to yana so ya zama malamin asibiti nan ma aka ce a’a sai dai ya yi aikin koyarwa a makaranta. Shi kuma bai cika son koyarwa ba.

Koyarwarsa:
Bayan ya gama kwalejin Kaduna ne, Malam Aminu Kano ya samu aikin koyarwa a makarantar Middle da ke Bauchi, inda a lokacin Sir. Abubakar Tafawa Balewa yake a matsayin Hedimasta, Daga Bauchi middle school sai aka canza wa Malam Aminu Kano wajen aiki zuwa kwalejin horar da malamai ta Maru dake Gundumar Sokoto a matsayin hedimasta a shekarar 1949 inda yayi shekara daya a nan kafin daga nan ya ajiye harkar aiki ya kama harkokin siyasa gadan – gadan.

Siyasa:
Gwagwarmayar Mallam Aminu ya fara ne tun yana dalibi a sakandare, Malam Aminu Kano ya fara sansanar harkokin siyasa ne tun a shekarar 1943 lokacin daya taimaka wa Malam Sa’adu zungur suka kafa wata kungiyar siyasa mai suna kungiyar cigaban Bauchi a jihar Bauchi a shekarar 1946.

Malam Aminu kano da Malam Sa’adu Zungur sune suka karfafa kafuwar jam’iyyar NORTHERN ELEMENT PROGRESSIVE UNION, (NEPU) wadda mutane 8 suka kafa a ranar 8 ga watan 8 a shekarar 1948. Duk da Cewar babu su a zaman tattaunawar ranar.

Malam Aminu Kano ya rungumi harkokin siyasa sosai wanda har hakan tasa ya ajiye aikin sa a ranar 4 ga watan nuwamba a shekara alif 1950. Shekaru 30 Mallam yana jam’iyyar adawa domin fafutukar samarwa talaka ’yanci, ya kubuta daga kangin danniya, zalunci da ake musu a lokacin mulkin mallaka na turawa da kuma bayan an samu ’yancin kai. Masana tarihi a kan rayuwar Mallam Aminu Kano sun ce Malam ya fara koya wa talaka yin tirjiya idan an zalunce shi, kana a karon farko talaka ya fara koyon cewa, a’a a ba ni hakkina a lokacin talakawa suna noma a gandun Sarki kyauta babu kudi.

Malam Aminu ya fara tsayawa takarar zabe na farko a jam’iyar NEPU a shekarar alif 1954 ya fadi zabe a kokarinsa na zama dan majalisar tarayya, Danmasainin Kano, Maitama Yusuf na jam’iyar NPC shi ya kada shi. A shekarar alif 1956 ya kuma kara shan kaye a zaben da ya shiga na majalisar dokokin jihar Arewa.

A shekarar alif 1959 zuwa 1966 ya ci zaben Dan majalisar tarayya inda ya wakilci Kano ta Gabas a karkashin Jam’iyar NEPU, shine mai tsawatar wa a majalisar hadin gwiwa, kuma ya rike kwamishan lafiya na tarayya kuma Dan majalisar zartarwa na koli a gwamnatin tarayya a lokacin mulkin Janar Yakubu Gowon.

A lokacin da sojoji suka karbi mulki, Malam Aminu ya yi ministan Lafiya a gwamnatin Yakubu Gawan tsakanin shekarar alif 1967~1974. A jamhoriya ta biyu a shekarar alif 1979 Malam Aminu ya tsaya takarar shugaban ƙasa a jam’iyarsa ta PRP, amma ya sha kaye a hanun Alh Shehu Shagari na NPN.

Gwagwarmayar Sa Da Turawa.
A karshe Mallam Aminu ya rubuta wani dan karamin littafi mai kunshe da raddi a kan bakin mulkin Turawa. Littafin da ya sanya wa suna {Kano Under the Hammer of the Native administration} duk da haka aka kara yi masa tayin samun malamin jami’a mai koyar da harshen Hausa a jami’ar Oxford da ke Ingila amma Malam Aminu yaki karba, Mallam Aminu ya bar aikin koyarwa ya kuma tsunduma harkokin siyasa gadan-gadan. Domin ita ce hanya kadai da zai bi ya kwato wa talaka ’yancin sa, ba tare da ya fuskanci barazana daga Turawan mulkin mallaka ba.

Malam Aminu Kano dashi akai ta gwagwarmaya wajen mayar da mulki ga hannun farar hula a zamanin Yakubu Gowon wanda Yakubun ya daga bayar da mulkin wanda a dalilin hakan ya haddasa hambarar da Gwamnatin Gowon din a shekarar 1975 inda Murtala Muhammed ya gaje shi. Da shi akai gwagwarmaya wajen mayar da mulki ga farar hula a shekarar 1979. Malam Aminu Kano shine shugaban jam’iyar PRP kuma dan takararta na shugabancin kasa a shekarar 1979.

Malam Aminu yayi kaurin suna wajen kin manufofin turawa dama duk wanda zai kawowa arewa wargi, mutum ne wanda bashi da kwadayi kuma baya siyasar kudi face akida zalla. Kuma makusantan sa wadanda suka yi tarayya da shi a siyasa suka ce a kullum tunaninsa idan garin Allah ya waye, bai wuce abu daya ba, wato yadda za a kyautata zaman jama’a.

Tunanin mutane tsakanin sa da Sardaunan Sokoto:
Wasu daga cikin mutane sun yi ta yayatawa tare da tunanin akwai rashin jituwa mai karfi tsakanin Malam Aminu Da Sardaunan Sakkwato Ahmadu Bello, da Tafawa Balewa, wannan zance bashi da tushe domin ko bayan rasuwar su an jiyo muryar Malam Aminu a laccoci daban – daban yana yabo da bayyana Sardauna a matsayin mutum mai Amana, Juriya, Jajircewa kuma ya yiwa Arewa abun da ba za’a manta dashi ba.

Tausayin Sa:

Adalcin Malam Aminu Kano bai tsaya ga mutane ba kawai, har ga tsuntsaye da dabbobi, shi yasa duk lokacin da yayi jawabi yana cewa jama’a ku yiwa dabbobi da tsuntsaye adalci domin akwai hakkinsu a wuyan mu. Misali wata rana Malam Aminu Kano ya Shiga cikin birnin Kano domin gabatar da ta’aziyya sai ya hangi wani dan kwuikwiyo a kwance tsananin yunwa ta sa ko tashi baya iya yi sai yara ne suke ta jagwal-gwala shi, sai Malam ya tsaya ya bayar da kudi yace a sayowa karen nan abinci, bayan ya dawo gida tunanin karen nan ya dame shi sai yace to gobe kuma waye zai bashi abinci? Dan haka yasa aka je aka daukko masa karen nan ya kawo shi gidansa har ya saka masa suna Jaura saboda lokacin ana cikin hunturun sanyi.

A takardar barin aikin Malam Aminu Kano da ya rubuta ranar 4 ga nuwamba 1950: “Na hango wani haske a can nesa tsakanin sama da ƙasa. Don haka zan yi kokari in riske shi, ko da a ce ni kadai ne ko da wani.”.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »