Takaitaccen Tarihin Zainab Sambisa.

0 3,651

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Zainab Usman Aliyu wacce aka fi sani da Zainab Sambisa yar wasan Kannywood ce, abin koyi, mawakiyar Hausa. An haife ta a jihar Gombe ta Najeriya.

Farkon Rayuwa da Sana’a

Zainab Sambisa ta taso tare da iyayanta. Ta kammala makarantar firamare da sakandare a jihar mahaifiyarta, jihar Gombe sannan ta koma jihar Kano inda ta shiga masana’antar shirya fina -finan Hausa.

Zainab doguwa ce,  kyakkyawa, kuma tana daya daga cikin fitattun jarumai a masana’antar fina-finan Hausa wato Kannywood.

Ana kallon Zainab a matsayin daya daga cikin fitattun jarumai a masana’antar Kannywood. Tun tana kuruciyarta tana da burin yin wasan kwaikwayo kuma yawancin fina-finan Hausa da take kallo sun zaburar da ita akan kudirinta.

Zainab Usman ta fara baje kolin wakokin Hausa tare da mawaka kamar; Hamisu Breaker, Garzali Miko, da sauran mawakan masana’antar Kannywood. Ta shahara ne da fara fitowa a waƙar Hausa mai suna “Sambisa” tare da mawaki “Ibrahim Yamu Baba”.

Ta samu laƙabin, “Zainab Sambisa” daga waƙarta ta farko mai suna ‘Sambisa’ wadda ke nuna ma’ana a wasan kwaikwayo da inganta sana’arta.

Ta fito a fina-finan Hausa da dama kamar; “Zaleehat” da “Fansar Kauna” a shekarar 2020.

A shekarar 2020 ta samu karin girma inda ta zama daya daga cikin fuskokin masu tallata masana’antar Kannywood kamar sauran jarumai mata.

A cikin 2021, an nuna Zainab a cikin bidiyon waƙar “TELA” tare da Yamu Baba.

Zainab Sambisa Musulma ce kuma ta fada a shafinta na Instagram cewa tana son mahaifiyarta fiye da komai a duniyar nan.

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »