Tarihin Mawaki Zayn Africa.

0 479

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

TARIHIN ABDULMAJID DA AKE KIRA DA ZAYNAFFRICA

Abdulmajid Aliyu (wanda aka fi sani da Zayn Afrika) mawakin gambarar Hausa ta zamani wato Hip-hop.

An haifi Zayn Afrika a garin Kaduna a ranar 1 ga watan Yunin shekarar alib 1994. Yayi Firamare da Sakandare a makarantar sojoji ta Command (CSSKD) da ke Kaduna.

Sannan ya wuce Karatun Digiri a fannin Kimiyyar Kwamfuta a Jami’ar Bayero da ke Kano.

Zayn Afrika ya fara wakokin Hip-hop a Kungiyar Yaran North Side (YNS) kafin daga bisani ya fara hadin gwiwa da wasu mawakan na Arewa kamar su Deezell da Classiq da Morell da sauran wasu fitattun mawakan Hausa na Arewa.

WAKOKIN DA ZAYN AFRICA YAYI.

Zayn ya yi wakokii masu yawa a Arewa daga cikin wakokinsa sun hadar da.

  • Don’t Cry
  • Don’t Cry: with Babsin
  • Kece On My Mind
  • Mamanmu
  • Mamanm: tare da DJ AB and Feezy
  • Kishiya: tare da Feezy
  • Kije Gida
  • You Want It: with DJ AB and Feezy
  • Ki Dawo
  • Banga Wata Ba

LAMBAR YABO DAYA SAMU.

  • A shekarar 2013, yasamu kyuatar Gwarzon Mawakan Arewa wato (Norther Nigeria Awards).
  • A shekarar 2017, yasamu kyautar Gwarzon Mawakin Kaduna wato (Kaduna Best Singer of the Year).

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »