TARIHIN SARKIN KANO USMAN MAJE RINGIM (1846)

0 1,563
Sarkin Musulmi  Aliyu Babba wanda ya kasance mai imani da bin adini ya nada shi Sarkin Kano a cikin Rabiul Auwal 1262 AH  wanda yay daidai da Maris 1846 AD

Shekaru ukun farko na mulkinsa sun kasance cikin kwanciyar hankali sannan kuma fitina ta bijiro ta fitaccen Malami wato  Hamza   wanda ya gayyato malaman tsibbu kamar sihiri don samun taimakon jahilai sannan kuma yana da manyan mabiya da suka haɗu da ɗalibai da ƙwararrun malamai.

Hamza da mabiyansa sun ki biyan haraji a wannan lokacin, Sakamakon wannan Sarki Usman ya umurce su da su bar yankin Kano.

Sun yi hijira zuwa Duwa ne inda  Dan Daura ke mulki, Dan Daura ya yi musu maraba da kyau. Daga baya Hamza ya sami goyon bayan Maguzawan garin inda yasamu damar  hambarar da Da Daura kuma ya zama Jagora na Maguzawan yankin. Mabiyansa suna kai hari kan lardunan makwabta na Sakkwato .

Barazanar ta gaba ga mulkinsa shine ci gaba da mamaye yankin Kano daga hannun azzalumai: Maiyaka Dan Yakubu, Sarkin Katsina da  na Maradi da Sarki Ibrahim na Zinder. Waɗannan azzalumai sun bautar da kashe yawancin musulmai kuma marayu sunyi yawa.

 A cewar Alkalin Kano Zangi an ci shi sau da yawa yayin mulkinsa,  Dokta Hienrich Barth, masanin binciken Turai wanda ya ziyarci Kano a wannan lokacin kuma ya tabbatar da rashin nasarar da Kano ta samu da kuma rauni na Sarkin Kano Usman .

Kano ta kasance cibiyar kasuwanci mai nagarta sosai wanda ke da mutane sama da dubu talatin (30,000)  a zamanin Sarki Usman. Dokta Barth ya bayyana Kano a matsayin kyakkyawar ƙasa mai wadata da “Lambun ta tsakiyar Afirka”. Babban kayan masarautar Kano shine auduga.

 Sauran kayayyaki daga Arewacin Afirka suma an samun  su a kasuwar Kurmi ta garin Kano. Wuri  shine kuɗaɗen yin kasuwanci  amma  kuma ana amfani da zinare a wajen yin cinikayya.

Kano ita ce “cibiyar kasuwanci” a kasar Hausa saboda haka Turawan mulkin mallaka na Turai suka kasa yin watsi da ita. Dalilin ziyarar Dr. Barth shine don yin bincike ƙasa don  Turawan mulkin mallaka na ƙasar Biritaniya a nan gaba.

Usman sarki ne mai matukar kulawa. Ya tura mafi yawan nauyin gudanarwar aiyukansa  ga dan’uwansa  Galadima Abdullahi, wanda kuma shine Waziri. Sauran manyan shugabanninsa sune Sarkin Bai Muhammad Kwairanga (wanda ya gaji mahaifinsa, Mallam Dabo Dambazau), Madaki Umaru Nayaya, masanin tarihi Alkalin Kano Muhammad Zangi, Sarkin Dawaki Abdu, Sarkin Dawaki Danladan da Dan Iya Lawal.

Sarkin Kano Usman ya mutu a ranar Lahadi 12th Dhi al-Hajj 1274 AH  wanda yay dai dai da 26th Agusta 1885 a Ringim Saboda haka ake masa laqabi da Maje Ringim ma’ana  (wanda ya mutu a Ringim).

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »