ASSALIN WASSAN BARKWANCI TSAKANIN KANAWA DA ZAZZAGAWA

0 835

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

 MA’ANAR WASAN BARKWANCI
Wasannin barkwanci wata hanya ce da Malam Bahaushe  ya kirkiro domin inganta dankon
 zamunci tsakanninsa da ‘yan  uwansa Hausawa dake zaune a wani yanki, ko kuma wata  kabila wadda ke mu’amilla dashi. Wasu daga cikin irin  wadannan wasanni na barkwanci sun samo asali ne ta faruwar  wani al-amari ko dai tsakanin Hausawa da wasu danginsu dake   zaune a wnai waje ko kuma tsakanin su da wasu kabilu da suke  cudedeniya.

ASSALIN WASAN BARKWANCI TSAKANIN KANAWA DA ZAZZAGAWA

 
Ance wai tun zamanin da, sa’ar da Sarkin Kano  Muhammadu Bugayya yahau karagar mulkin kano a  shekara ta 1386 bayan mutuwar Sarkin Kano Aliyu Yaji  dan Tsamiya aka soma wasan gargajiya tsakanin kanawa  da zage-zage.

Asalin abin akace watarana ne Sarkin Kano Bugayya ya  fita yaki zuwa kasar Zazzau, ya tafi da jarumawan sa  masu yawa ya doshi garin Turunku birnin Zazzagawa.

Tun kafin ya riski garin sai labari ya iske sarkin Zariya na  lokacin Muhammdu Abu cewa ga kanawa nan suna zuwa  Zazzau da yaki.

Wai dajin haka sai Sarkin Zazzau ya tara mayakansa suka  dunguma zuwa wani wuri mai suna kufaina da shirin yaki,  da zimmar su tari kanawa tun kafin su karaso Turunku.  Da zuwa sai suka hau saman dutsen Kufaina suna jiran  kanawa.

Lokacin da kanawa suka iso, tun daga nesa suka hango  dakarun Zazzau a saman dutse, don haka kai tsaye sai  suka tunkari gindin dutsen, sai jiyo mai shela akayi  acikinsu yana shelanta cewa duk mutumin Kano ya nada gammo, zamu taru mu dauki dutsen kufaina tare da  mutanen dake kansa mu tafi dasu Kano da sauri.

 Daga  nan sai kurum akaji kanawa sun dauki sowa suna fadin  hobbasa! Hobbasa! Hobbasa! Akace dajin haka sai Sarkin Zazzau Muhammadu Abu  yace ga mayakansa “Yaku Jaruman Zazzau, kada kowa ya  motsa, wannan zambo ne na kanawa barayi mazambata.  Ko aljanu basu iya daukan dutsen nan in ba mala’iku ba”.

Kunsan Zazzagawa (ga tsoro, kuma ba wayau), sai sukaki  jin umarnin sarkin su. Suka rinka tsalle daga can  kololuwar dutse suna tumowa kasan dutse, jikake tim.  Wasu suka fado matattu, wasu kuma suka fado karyayyu,

wadansu kuma basu karye ba amma dai sun suma.  Kanawa na ganin haka sai suka tattara sumammun da  karyayyun sukayi awon gaba dasu izuwa Kano, akabar  matattu yashe a gindin dutse, acan aka maishe su bayi  bayan sun murmure.

Acan birnin Turunku kuwa, bayan kanawa sun janye  jikinsu daga kasar Zazzau, sai Sarki Muhammadu Abu ya  tarasu, yayi musu fada da gargadi akan kin bin umarninsa  da sukayi. Yake cewa ku Zazzagawa kun bani kunya, me  yasa kuka ki jin magana ta kukayi ta tsalle kuna fadowa  gaban kanawa mazambata?

Anan ne sai wasu daga mayakan Zazzagawa suke cewa  Ran sarki ya dade, yayin da mukaji kanawa na fadin  hobbasa, sai mukaji tamkar sun daga dutsen, suna tafiya  dashi izuwa kano. Mu kuma sai mukayi ta tsalle don bama  so kanawa su tafi damu kano. Sai sarki yace wannan ai zambo ne irin na barayi.

Ance tun daga wancan lokaci aka samo wasan gargajiya  wanda akeyi tsakanin Kanawa da zage-zage.

………..
Daga
LITTAFIN TASIRIN MAWAKAN BAKA WAJEN HABAKA AL-ADUN HAUSA
NA IBRAHIN MUHAMMAD

Get real time updates directly on you device, subscribe now.

Leave A Reply

Your email address will not be published.

Translate »